5 February 2016

[Kannywood] Gwamnan Jihar Kano Yabawa Jarumar Shirin Hausa Mukami Wato Rashida Sa'a


Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya baiwa fitacciyar jarumar finafinan Hausan nan, Rashida Adamu mukamin mai taimaka masa kan harkokin da suka jibanci mata a jihar.

Jarumar wadda ake yi wa lakabi da Rashida Mai Sa'a, bayan ta nuna farin cikinta ga wannan matsayi da gwamnan ya ba ta, ta kuma yi kira ga al'umma da su taimaka mata da addu'a don ganin ta tafiyar da matsayin da aka ba ta cikin nasara, sannan kuma ta nemi su ba ta shawarwarin da za su taimaka mata wajen gudanar da ayyukanta.



0 comments

Post a Comment